musulmi - Shafi 22

IQNA

Tehran (IQNA) Sir Lindsay Hoyle, kakakin majalisar dokokin kasar Birtaniya, ya karbi bakuncin gungun wakilan musulmi na majalisar dokokin kasar, da fitattun masu rike da madafun iko, da kuma wasu al’ummar musulmin kasar nan a wajen buda baki na wannan majalisa.
Lambar Labari: 3488900   Ranar Watsawa : 2023/04/01

Rahamar Allah tana gudana a cikin dukkan abubuwa da abubuwan da suke faruwa a duniya, kuma babu wani abu a duniya da ba ya karkashin rahamar Ubangiji, kuma ko shakka babu sharadi na samun rahamar Ubangiji na musamman shi ne tuba da neman gafara.
Lambar Labari: 3488887   Ranar Watsawa : 2023/03/29

Tehran (IQNA) Dakarun mamaya sun kai farmaki ne da asuba a yau litinin, a harabar masallacin Al-Aqsa da masallacin Al-Qibli, inda suka kai auka kan masu ibada da karfin tsiya.
Lambar Labari: 3488875   Ranar Watsawa : 2023/03/27

Sakataren kwamitin muslunci na kasar Spain, yayin da yake jaddada gagarumin ci gaban al'ummar musulmi a wannan kasa cikin shekaru 30  da suka gabata, ya bayyana cewa: Musulman kasar Spain suna isar da sakon jaddada hadin kai na addini ta hanyar shigar da makwabtansu wadanda ba musulmi ba a cikin bukukuwan watan Ramadan.
Lambar Labari: 3488869   Ranar Watsawa : 2023/03/26

Tehran (IQNA) Bayan kimanin watanni 18, wani kamfani na kasar Ingila a birnin Bradford ya yi nasarar kera wani murfin da ya dace da amfani da mata musulmi a cikin 'yan sanda.
Lambar Labari: 3488866   Ranar Watsawa : 2023/03/26

Sakon fadar Vatican kan lokacin watan Ramadan;
Tehran (IQNA) Ta hanyar buga saƙon watan Ramadan da Eid al-Fitr, hedkwatar tattaunawa tsakanin addinai ta Vatican ta nemi Kiristoci da Musulmi a faɗin duniya da su haɗa kai don samar da zaman lafiya da jituwa tare da adawa da al'adun ƙiyayya.
Lambar Labari: 3488864   Ranar Watsawa : 2023/03/25

Teharan (IQNA) Musulmi a birnin Nairobi, babban birnin kasar Kenya, sun kaddamar da wani shiri na taimakon mabukata tare da raba kayan abinci ga mabukata.
Lambar Labari: 3488862   Ranar Watsawa : 2023/03/25

Tehran (IQNA) Dalibai a jami'ar Wisconsin da ke kasar Amurka na yin taruwa a cikin wadannan kwanaki domin murnar ganin watan azumin Ramadan.
Lambar Labari: 3488857   Ranar Watsawa : 2023/03/24

Tehran (IQNA) Kungiyar kwallon kafa ta Brighton ta kasar Ingila ta gayyaci musulmai da su halarci bukin buda baki a filin wasa na kungiyar a mako mai zuwa.
Lambar Labari: 3488848   Ranar Watsawa : 2023/03/22

Tehran (IQNA) Rundunar ‘yan sandan Biritaniya ta sanar da neman mutumin da ya kai wa wani mai ibada hari a Birmingham, wanda ya yi sanadiyyar kona tufafinsa.
Lambar Labari: 3488846   Ranar Watsawa : 2023/03/21

Tehran (IQNA) Yayin da watan Ramadan ke gabatowa, musulman kasar Canada suma suna shirye-shiryen gudanar da ayyukan wannan wata. Musulman birnin Montreal ma sun yi maraba da wannan wata mai alfarma ta hanyar kafa kasuwar bajekoli ta Ramadan.
Lambar Labari: 3488845   Ranar Watsawa : 2023/03/21

Tehran (IQNA) Hotunan Sadio Mane dan kasar Senegal na kungiyar Bayern Munich, yana karatun kur'ani ya samu karbuwa daga wajen musulmi masu amfani da shafukan sada zumunta.
Lambar Labari: 3488838   Ranar Watsawa : 2023/03/20

Tehran (IQNA) Kungiyar kwallon kafa ta Aston Villa ta sanar da cewa za ta gudanar da bukin buda baki ga jama'a a filin wasanta na wannan watan Ramadan.
Lambar Labari: 3488824   Ranar Watsawa : 2023/03/17

Tehran (IQNA) Kwanaki kadan gabanin fara azumin watan Ramadan daya daga cikin shugabannin na hannun daman Faransa ya soki yadda ake samar da kayayyakin halal a shagunan kasar tare da bayyana hakan a matsayin wani yunkuri na musuluntar da kasar Faransa.
Lambar Labari: 3488823   Ranar Watsawa : 2023/03/17

Tehran (IQNA) A yayin cika shekaru hudu da harin ta'addancin da aka kai a wasu masallatai biyu a birnin Christchurch na kasar New Zealand, musulmi da jami'an kasar sun jaddada wajibcin yaki da tsatsauran ra'ayi da kyamar Musulunci.
Lambar Labari: 3488817   Ranar Watsawa : 2023/03/16

Tehran (IQNA) Firaministan Malaysia ya kare dala miliyan 2.2 da aka ware domin buga tafsirin kur'ani da nufin yaki da kyamar Musulunci.
Lambar Labari: 3488740   Ranar Watsawa : 2023/03/02

Tehran (IQNA) A karon farko an nada wani musulmi farar hula a kwamitin sa ido na 'yan sandan New York.
Lambar Labari: 3488734   Ranar Watsawa : 2023/02/28

Tehran (IQNA) Musuluntar da wani fitaccen Fasto Ba'amurke ya yi, ya yi tasiri sosai a cikin mabiya addinin Kirista da na Musulunci.
Lambar Labari: 3488732   Ranar Watsawa : 2023/02/28

Tehran (IQNA) A yayin da aka gano gawarwakin wasu Musulman kasar biyu a jihar Haryana, jama'a sun nuna fushinsu ga gwamnatin Indiya saboda nuna halin ko in kula da kai hare-hare kan musulmi tsiraru na kasar.
Lambar Labari: 3488685   Ranar Watsawa : 2023/02/19

Tehran (IQNA) A ranar 5 ga watan Maris ne za a gudanar da taron tattaunawa na addini tsakanin Musulunci da Kiristanci, a karkashin inuwar hukumar kula da al'adu ta Iran a kasar Zimbabwe, a jami'ar "Turai" da ke birnin Harare.
Lambar Labari: 3488683   Ranar Watsawa : 2023/02/19