IQNA

Hukumar WHO: Bayyana Cutar Corona Da Cewa Cuta Ce Da Ta Mamaye Duniya Ba Gaskiya Ba Ne

23:52 - February 26, 2020
Lambar Labari: 3484564
Tehran - (IQNA) babban daraktan hukumar lafiya ta duniya WHO ya bayyana cewa, kiran cutar corona da cewa cuta ta mamaye duniya wannan tsorata al'ummomin duniya ne kawai.

Tashar Russia Today ta bayar da rahoton cewa, Tedros Adhanom babban daraktan hukumar lafiya ta duniya WHO ya bayyana cewa, yin amfani da kalmomi da ke nuni da cewa cutar corona ta mamaye duniya, suna saka tsoro da firgici a cikin zukatan mutane a duniya.

Ya kara da cewa, yin amfani da irin wadannan kalmomi za su sanya ayi zaton cewa hukumomin lafiya na kasashen sun gaza wajen tunkarar wanann cuta, wanda kuma ba haka ba ne, domin kuwa suna yin iyakacin kokarinsu.

Haka nan kuma babban daraktan na hukumar lafiya ta duniya ya nuna damuwa kan yaduwar cutar a kasashen  Koiya ta kudu da Italiya da kuma Iran.

 

3881688

 

 

captcha