IQNA

Nasrallah: Ashura A Bana Za Ta Hada Da Juyayin Kisan Al’ummar Yemen

23:14 - October 11, 2016
Lambar Labari: 3480845
Bangaren kasa da kasa, babban sakataren kungiyar Hizbullah ya bayyana taron da za a gudanar da Ashura a bana da cewa zai hada da alhinin kisan bayin Allah da masarautar Saudiyyah ta yi a Yemen.
Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqn aya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na tashar alalam cewa, Sayyid Hassan Nasrallah babban sakataren kungiyar Hizbullah ya bayyana cewa Ashura ta bana zata yi alhinin kisan bayin Allah da masarautar Saudiyyah ta yi a Yemen a wannan mako.

Sayyid Nasrullah ya bayyana cewa kisan gillar da masarautar ‘ya’yan Saud ta yi a kan fararen hula a ranar asabar da ta gabata a birnin San’a na kasar Yemen aiki ne na dabbanci da rashin imani.

Ya ce hakika abin kunya ne ga masu ikirarin cewa suna kare martabar haramomi masu tsarki guda biy su aikata danyen aiki na kisan gilla a kan fararen hula musulmi a cikin wannan wata wanda aka haramta zubar da jinni a cikinsa.

Sayyid Nasrullah ya ce a wannan shekara tarukan ashura a ranar goma ga watan muharram za su hada da juyayin ashura da kuma kisan kiyashin da aka yi wa musulmi a Yemen a hannun mashaya jini masu kwadayin zubar da jini na bayin Allah.

Wanann mataki shi ne irinsa da kungiyar Hizbullah ta dauka a lokacin da yahudawan sahyuniya suke ruwan bama-bamai a kan al’ummar yankin zirin Gaza, inda aka gudanar da Ashura tare da yin juyayi da alhini kan kisan kiyashin da Isra’ila take kan al’ummar Gaza a lokacin, wanda kuma a wannan karon masarautar Saudiyya ce take tafka irin wannan aiki na Isra’ila amma a kan al’ummar Musulmi na Yemen.

Sayyid Nasrullah ya ce yan akira ga wadanda za su fita aranar Ashura da su daga tutocin Imam Hussain (AS) a lokaci guda kuma su daga totocin kasar Yemen, domin nuna goyon bayansu ga musulmin Yemen da Saudiyya ke ma kisan kiyashi.

3537272


captcha